Sunday, July 1, 2012

Kwallon Kafa: Siasia Yana Karbar Albashin Mutum 277



Kwallon Kafa: Siasia Yana Karbar Albashin Mutum 277
Najeriya a harkar kwallon kafa a shekarun baya ba kanwar lasa ba ce. Don idan muka tuna lokacin da akayi gasar cin kofin duniya a shekarar 1994 a kasar Amurka, Najeriya ta taka rawar gani sosai domin ta samu tsallakewa daga rukuni har takai matsayin kwata final, kafin a fitar da ita daga wannan gasa, irin rawar da Najeriya ta taka a wannan gasa ta 1994, ya kara mata kima da daraja a idon duniya sosai da sosai, wannan ta sanya Najeriya baza ta manta da manyan 'yan kwallon da suka yi kwallo ta kishi ba irinsu Tijjani Babangida da Garba Lawal da Emmanuel Amonike da Ikedia da Austin Eguavoen da Kanu Nwankwo da Sunday Olushe da marigayi Rasheedi Yakini da kuma tsohon mai tsaron gida wato Peter Rufai da sauransu da dama.
Sunan Najeriya bai kara daukaka ba a harkar kwallon kafa sai a gasar Atlanta 1996, inda Najeriyar ta lallasa kasar Brazil a wasan karshe, wanda wannan ya baiwa Najeriya nasarar zamowa zakara, wannan nasara da Najeriya ta samu ta bangaren dan wasan ta Kanu Nwankwo hakika babbar nasara ce da ba'a taba tsammani ba, domin kuwa kowa yasan yadda kasar Brazil take a harkar kwallon kafa, tun bayan wannan gasa ce sunayan mutane irinsu Daniyal Amokashi da Kanu Nwanko da Jay Jay Okosha suka yi suna a duniya, duk sadda dan Najeriya ya fita zuwa kasar waje sai kaji ana tambayarsa ya labarin 'yan wasan Najeriya wadan da muka lissafa.
Sannan sunan Najeriya ya buwaya a kasashen Afurka baki daya ta fannin kwallon kafa, domin duk fadin Nahiyar babu 'yan wasan da suka kai na Najeriya iya taka leda, duba da irin nasarar da suka ringa samu ta lashe gasar cin kofin Nahiyar Afurka, wannan ya karawa sunan Najeriya martaba sosai a kasashen Afurka ta fannin tamaula.
Haka kuma, a gasar cin kofin duniya na shekarar 1998 da akayi a kasar Faransa wannan ma 'yan wasan Najeriya sun yi rawar gani. Domin sun kai wasan kusa da nakusa da na karshe, kusan zamu iya cewa tundaga wannan shekara ce Najeriya ta fara komawa baya a harkar kwallon kafa, kafin daga bisani ta durkushe baki daya.
Wani abin mamaki shi ne, babu wani abu da yake hade kan 'yan Najeriya waje daya kamar kwallon kafa, hakika duk lokacin da ake yin kwallo da Najeriya zaka sha mamakin ganin yadda 'yan Najeriya ke fatan alheri ga tawagar Super Eagles, babu maganar kudu ko Arewa Musulmi ko Kirista kowa murna yake yi idan aka samu nasara, haka kuma zaka ga 'yan Najeriya cikin damuwa sosai idan aka lallasa Najeriya babu maganar Bahaushe ko Beyerabe ko Inyamuri kowa nuna damuwa yake yi.
Haka kuma, idan ka shiga gidan kallon kwallo a lokacin da ake yin kwallon kafa da Najeriya, zaka ga yadda kusan dukkan kabilun Najeriya ke haduwa ana raha da juna a gidajen kallon kwallo, babu maganar wane ba wane ne ba, idan kuwa akaci nasara kaga bahaushe ya rungume beyerabe bafulatani ya rungume inyamuri ana murna ana sowa da nasarar da wannan kasar tamau ta samu.
Harkar kwallon kafa yanzu a Najeriya kusan zamu iya cewa ta zama tarihi. Shakka babu bazai zama kuskure ba idan mutum yace kwallo ta zama tarihi a halin yanzu, sai dai a baiwa yara na baya labarin irin kokarin da 'yan kwallonmu sukayi a baya, babu batun babban kulab na kasa Super eagles ko Flying Eagles ko Super Falkons ko matasa 'yan kasa da shekaru 20 ko 18 da dai sauransu kusan gabaki daya harkar wasanni ta koma baya, kuma irin kishi da dokin da 'yan Najeriya suke dashi a harkar kwallon kafa kusan shima zamu ce ya zuwa yanzu kusan ya zogaye fiye da yadda aka sanshi; da gwamnatin Najeriya da gaske take akan hadin kan kasarar nan da batayi sake da harkar wasanni ba, domin kamar yadda muka fada babu wani abu kaf Najeriya da yake hada kan 'yan kasa kamar wasan kwallon kafa ko kuma kace Super Eagles, amma akayi sakaci da wannan dammar da gangan ta zogaye a banza.
Tsohon dan wasan Najeriya a shekarun da suka gabata Samson Siasia yanzu shi ne mai horas da 'yan wasan super Eagles kulab din da ya taba bugawa kwallo. Sai muce Najeriya bata taba samun koma baya ba a harkar kwallon kafa kamar yadda ta ke samu a yanzu karkashin kulawar Siasia wanda yana daya daga cikin Wadan da suka fito da sunan Najeriya a harkar kwallon kafa a shekarun baya, duk kuwa da irin makudan kudin da yake karba a matsayin albashi, kamar yadda majalisa tayi doka cewar mafi karancin albashi a gwamnati shi ne Naira 18,000 kusan zamu ce Siasia yana karbar sama da albashin mutum 277 don yana karbar kusan Naira Miliyan 5,000,000 a duk watan duniya da sunan mai horas da 'yan wasan Najeriya.
Haka kuma, kungiyar ta super Eagles har yanzu ta kasa tabuka wani abin kirki a karkashin kwac Siasia domin har yanzu ko kwalba basu dauko mana ba da sunan samun nasara, harkar siyasa da kabilanci kusan zamu iya cewa su ne ummul haba'isin durkushewar harkar wasanni a Najeriya, domin akwai 'yan wasa wadan da suka iya kuma suka cancanta amma saboda kabilanci sai a kyalesu a dauki wadan da basa iya tabuka komai sai kashe musu kudi da akeyi ana zagayawa da su yawan buda ido da sunan kwallo. Lallai ya kamata hukumar NFF su yi dukkan mai yuwuwa wajen kawo gyara a harkar wasanni a Najeriya.
Muna fatan watan wata rana sunan Najeriya ya sake buwaya a harkar kwallon kafa a duniya, ina burin ganin lokacin da kulab din Super Eagles zasu ciwo gasar kofin duniya su zo da shi Najeriya su zagaya da shi Najeriya gabaki daya, inama zan samu damar dazan daga wannan kofi domin nuna murna da nasarar da kasata ta samu a gasar cin kofin duniya, lallai ina fatan ganin wannan ranar, Allah ya nuna mana da alheri.
Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment